MAKIRCIN SHAIƊAN MAFI GIRMA GA ƊAN ADAM



Daga shafin Bashir Halilu.

-  ﴿ مكيدة الشيطان الكبرى  ﴾ 
 
     قَالَ ابْنُ أَبِي الدُّنْيَا : حَدَّثَنَا أَبُو سَلَمَةَ الْمَخْزُومِيُّ، حَدَّثَنَا ابْنُ أَبِي فُدَيْكٍ، عَنِ الضَّحَّاكِ بْنِ عُثْمَانَ، عَنْ هِشَامِ بْنِ عُرْوَةَ، عَنْ أبيه، عن عائشة رضي الله عَنْهَا : عَنِ النَّبِيِّ صَلَّى اللَّهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ قَالَ: 
إِنَّ الشَّيْطَانَ يَأْتِي أَحَدَكُمْ فَيَقُولُ مَنْ خَلَقَكَ؟ 
فَيَقُولُ اللَّهُ تَبَارَكَ وَتَعَالَى.
 فَيَقُولُ مَنْ خَلَقَ اللَّهَ؟
 فَإِذَا وَجَدَ أَحَدُكُمْ ذَلِكَ فَلْيَقُلْ: 
آمَنْتُ بِاللَّهِ وَرَسُولِهِ فَإِنَّ ذَلِكَ يُذْهِبُ عَنْهُ.
 

   Ibnu Abid-Dunyā, a cikin littafinsa Maka'idush Shaiɗan, ya ruwaito cewa: Abū Salamatal -Makhzūmīy ya ba mu labari, ya ce: Ibnu Abī Fudayk ya ba mu labari daga Ḍhaḥḥāk bin ‘Usmān daga Hishām bn ‘Urwah daga mahaifinsa (Urwah), daga Nana A’isha – Allah ya yarda da ita – ta ce:

Manzon Allah ﷺ ya ce:

“Lallai Shaiɗan yana zuwa wurin ɗayanku ya ce masa: Waye ya halicce ka? 

Sai ya ce: Allah Mai girma da ɗaukaka.

    Sai ya ce masa: To wa ya halicci Allah?”

  *To idan ɗayanku ya sami irin wannan (waswasi), to ya ce: "Amantu billahi wa RasuwliHi" domin lallai wannan yana kore (waswasi) daga gare shi.”
 ❋・────━【❆】━────・❋

Daga shafin Bashir Halilu

Comments

Popular Posts