AIKIN SAƁON DA SHAIƊAN YA FI SO YA SAKA MUSLMI

Daga shafin Bashir Halilu 
     Ibni Abid dunya ya ruwaito cewa:  Al-Qurashiy ya ce: Ahmad bin Jameel Al-Marwazi ya ba ni labari, ya ce: Ibnul-Mubarak ya ba mu labari, ya ce: Sufyan ya ba mu labari daga Aɗā’ binis-Sā’ib daga Abū ‘Abdir-Raḥmān as-Sulamī daga Abū Mūsā (Allah ya yarda da shi) ya ce

     “Idan Iblis ya wayi gari, sai ya baza sojojinsa a doron ƙasa, sai ya ce: 

‘Wane ne ya ɓatar da wani Musulmi?, zan sa masa kambun sarauta’

    Sai ɗaya daga cikinsu ya ce: ‘Ban bar wane ba sai da ya saki matarsa.’
Sai Iblis ya ce: 

‘Ai zai iya sake aure.’

      Sai wani Shaiɗanin ya ce: ‘Ban bar wane ba sai da ya saba wa iyayensa.’

Sai Iblis ya ce:

 ‘Ai zai iya yi musu biyayya daga baya.’

       Sai wani ya ce: ‘Ban bar wane ba sai da ya yi zina.’

Sai Iblis ya ce: ‘Kai ne!’

       Sai wani ma ya ce: ‘Ban bar wane ba sai da ya sha giya.’

Sai Iblis ya ce: ‘Kai ne!’

     Sannan wani ma ya ce: ‘Ban bar wane ba sai da ya kashe wani.’

     Sai Iblis ya ce: ‘Kai ne! Kai ne! (Kai na fi so!)’
   Duba littafin Maka'idish Shaiɗan.

      Daga shafin Bashir Halilu.

Comments

Popular Posts