DUK WANDA YA ƘIRƘIRO SABUWAR IBADA TO BA SHI DA LADA


عَنْ أمِّ المُؤمِنينَ أمِّ عبْدِ اللهِ عائشةَ رَضِي اللهُ عَنْهَا قالَتْ: قالَ رسولُ اللهِ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ:

{مَنْ أَحْدَثَ فِي أَمْرِنَا هَذَا مَا لَيْسَ مِنْهُ فَهُوَ رَدٌّ}

رواه البخاريُّ ومسلمٌ.

وفي روايةٍ لمسلمٍ: {مَنْ عَمِلَ عَمَلاً لَيْسَ عَلَيهِ أَمْرُنا فَهُوَ رَدٌّ}.
An karɓo daga Ummul-Mu’uminina, Ummu Abdullahi, Nana A’isha (Allah Ya yarda da ita), ta ce: Manzon Allah ﷺ ya ce:

“Duk wanda ya ƙirƙiri wani abu a cikin wannan al’amari na mu (addininmu), wanda ba daga cikinsa ya ke ba, to abun juyarwa ne.”

    ★Wato dukkan wanda ya ƙirƙiro wani aiki na ibada wanda ba musulunci ne ya yi umarni ba to za a mayar masa da aikinsa, Allah ba Zai karɓa ba ballantana Ya ba shi lada.

(Bukhari da Muslim suka ruwaito shi.)

A wata ruwaya daga Muslim kuma:

Manzon  Allah Sallallahu alaihi Wasallama ya ce:

“Duk wanda ya aikata wani aiki wanda ba bisa umarninmu ba ne, to ba a karɓa.”

     ★Ma'ana aikin ibada wanda Allah da Manzonsa ba su ce a yi ba.

    Allah Ya raba mu da bid'ah, Ya ba mu ikon riƙo da sunnah kuma Ya tabbatar da mu akan imani.

Daga Shafin Bashir Halilu

Comments

Popular Posts